-Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karba bakuncin shugaban kasar Guinea Bissau
-Ya karbesa ne a fadar Aso Villa da ke babban birnin tarayyar Abuja, Najeriya
Kamar yadda hotunan suka nuna, shugabannin sun kiyaye dokar nesa-nesa da juna Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karba bakunci Shugaban kasar Guinea Bissau, Umaro Sissico Embalo a yau Asabar.
Ya karbesa ne a gidan gwamnatin tarayya da ke Aso Villa a babban birnin tarayyar Abuja. Kamar yadda hadimin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad, ya wallafa a shafinsa na Twitter, an ga shugabannin kasashen biyu suna biyayya ga dokar nesa-nesa da juna.
Shugaba Buhari ya karba samfur din maganin cutar korona na gargajiya na kasar Madagascar daga hannun shugaban kasar Guinea Bissau. Kasar Afrikan ta yi ikirarin cewa maganin na da karfin kashe kwayar cutar Korona.
Shugaba Buhari ya karba bakuncin Shugaban kasar Guinea Bissau.
DUBA WANNAN: Mutuwar ban mamaki: Wani mashahurin sarki ya mutu a Kano
biyu Shugaba Buhari ya karba bakuncin Shugaban kasar Guinea Bissau.
A yayin bayani a kan maganin, mai bada shawara na musamman ga shugaban kasa Muhammadu Buhari, Mallam Garba Shehu, ya ce Buhari ya tabbatar da cewa zai yi biyayya ga kimiyya kafin fara amfani da maganin. Babu dan Najeriya da zai yi amfani da maganin har sai an tabbatar da ingancinsa a kimiyyance..
“Kamar yadda shugaba Buhari ya tabbatar wa da Shugaba Umaro Sissioco na kasar Guinea Bissau, ya ce ba za a fara amfani da maganin gargajiyar har sai an tabbatar da ingancinsa,” Garba Shehu yace.
“Muna da dokoki da tsarika a kasar nan. Duk wani ikirari ko magani da aka aiko da shi kasar nan, hukumomi za su tabbatar da ingancinsa. Ba zamu fara amfani da maganin ba har sai sun tabbatar da ingancinsa,” Shugaba Buhari yace.
A wani labari na daban, gwamnatin jihar Katsina ta dage dokar kulle da ta saka a baya a kananan hukumomin Mani da Safana a jihar kamar yadda This Day ta ruwaito.
Gwamnan jihar, Aminu Bello Masari, ya amince da dage dokar zaman gidan nan take kamar yadda yake cikin sanarwar da sakataren gwamnatin jihar, Dr Mustaha Inuwa ya fitar.